Thursday, 26 January 2017

JAM'IYYAR APC TA GAYYACI SHEHU SANI KAN SUKAR BUHARI DA YA YI


Shugaban jam’iyyar APC na kasa baki daya, Cif John Odigie-Oyegun ya rubuta wata wasika a yammacin jiya wanda za’a aika ga sanatan na gayyatar sa hedkwatan jam’iyyar a Abuja don tattauna sukarsa ga yadda shugaban kasa ya dauki al’amarin zargin rashawa da ake yi a kan Lawal.

Kimanin wata daya da ya wuce, kwamitin kula da wadanda rikin Boko Haram ta cika dasu na majalisar dattawa karkashin jagorancin Sani ta zargi Lawal da aikata zamba na kwangilar sansanin yan gudun hijira a arewa maso gabas.

A wasikar sa ga majalisa, shugaban kasa yayi mamakin yadda akayi majalisar ta yanke shawarar kira ga cire Lawal alhalin ba’a taba kiran babban sakataren na tarayya don kare kansa ba.

No comments:

Post a Comment