Wednesday, 21 December 2016

FASTO YA YI WA 'YAR SA MAI SHEKARU 16 CIKI

Wani mutum dan shekaru 56, da haihuwa, wanda ke wa'azi a wani Coci, dake yankin Obodo, a jihar Ondo ya yi wa 'yar sa, yar shekara 16, ciki.

Mutumin wanda yanzu haka ke fuskantar bincike a wajen 'yan sanda, ya ce shedan ne ya ingiza shi har ya aikata wannan aikata-aika.

Wasu mazauna Unguwar,  sun shaida cewa, mutumin ya yi hakan ne, domin kara karfin ayyukan siddabaru da yake yi.

Malamin addinin Kiristan dai ya shahara, wajen yiwa mata a kududdufi,  wanka domin korar shaidanun da suka hana su aure.

Rahotanni sun ce a kwanakin baya ne, Faston ya rabu da matarsa, inda ta yi kokarin daukan yarinyar ta tafi da ita,  amma mutumin ya hana.

No comments:

Post a Comment